Uncategorized

Yadda Asirin Wani Malamin Makaranta Wanda Sha’awarsa Ke Tashi Duk Lokacin Da Yaji Muryar Dalibarsa Ya Tonu

Kamar yadda muka samo wata ɗaliba da ta shaidawa BBC Hausa irin kalubalen da ɗalibai mata ke fuskanta daga wajen malaman su da zummar basu damar cin jarabawa a karatunsu.

Ɗalibar ta koka sosai akan yadda wani malamin su ya ci zarafin ta, inda ya dinga neman ya yi lalata da ita tare da yi mata alkawarin taimakata wajen cin jarabawa.

Ta ce malamin yana fadamata cewa duk lokacin da yaji muryarta sai sha’awar sa ta motsa. Hakan yasa ya kasa yin hakuri.

Ta ƙara da cewa yana yawan yi mata irin wannan zancen, yana cewa wai in taimaka masa in biya mashi bukatarsa shima zai biyamin bukata ta.

Ɗalibar ta ce irin wannan yana faruwa sosai a dukkan makarantun gaba da sakandare ba kawai iya jami’a ne ba. Domin ɗalibai da dama suna yawan fuskantar irin wannan matsalolin.

Ɗalibar da ba’a bayyana sunanta ba saboda tsaro, ta ce dalibai mata da yawa suna rasa budurcinsu da Mutuncin su a dalilin cin zarafin da malamai suke yi musu.

Tace lamarin yana faruwa sosai a dukkan makarantu na gaba da sakandare kuma bazaka iya ware wasu rukunin mata ba ace sune aka fi yiwa hakan. Sannan kuma kaso 70% cikin 100% suna fuskantar wannan cin zarafi.

Mr.Bangis

Take Your Time And Come Back Strong!!!

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
×