Labaran Duniya

Alfarma; Muke Nema Buhari Yasaka Hannu A gina Jami’a A Funtua (Bello Mandiyya)

Shugaba Buhari Ka Taimaka Mana Ka Sanya Mana Hannu A Gina Jami’a a Funtua

Daga Ibrahim Auwal Al’ja,a Funtua

Yau sama da shekara daya kenan Majalisar Dattawa ta kasa a Nijeriya ta tantance tare da amincewa da gina Jami,ar Aikin Gona da Fasaha a Funtua, wanda Sanatan Shiyyar Funtua Sanata Bello Mandiya ya gabatar.

 

 

Bayan Majalisar Dattawa ta gama tantancewa, ta aikawa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Takardar domin Amincewa.

A yanzu haka Takardar na ofishin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari bai sanya hannu ba.

A madadin Matasa masu kishin Al,ummar Shiyyar Funtua, bisa jagorancin Malam Auwal Al’ja,a Funtua, muna koro da a taimaka a sanya mana hannu domin tabbatar da wannan Makaranta.

Mr.Bangis

Take Your Time And Come Back Strong!!!

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
×